Isma’il Dan Buran Lakwaja ya rasu @74

Daga Musa Tanimu Nasidi

Allah ya yi wa Alhaji Isma’il Abdukareem Dan Buran na Lakwaja rasuwa.

Abdukareem ya rasu yana da shekaru 75 a duniya a asibitin kasa Abuja a ranar Laraba 6 ga watan Agusta, 2025 bayan ya sha fama da jinya.

Tsohon kwamishinan INEC kuma wani lokaci mai kula da ayyuka a rusasshiyar karamar Hukuman Kogi, ya bar mata biyu da ‘ya’ya da jikoki.

Za a tuna da marigayi Dan Buram bisa sadaukar da kai ga al’ummar Lakwaja.

Allah ya gafarta masa dukkan kurakuran sa, ya saka masa da janadul-firdaus, ya baiwa iyalai da al’ummar Lokoja da daukacin al’ummar musulmi kwarin gwuiwar jure rashin da ba za a iya maye gurbinsa ba. Ameen.

Visited 13 times, 1 visit(s) today
Share Now
See also  Kogi Assembly Service Commission Chairman Mourns the death of John Abah